WAƘAR KYAUN ALƘAWARI



Ina maka sallama

Ya Baba Buhari miji ga Indo


Na zo ni da lalama

Amsa mini, kar da ka sa ni kwando


Tuni na taho na ma

Ƙafa ɗaya kar mu saka a wando


Waɗanda ka kai sama

Babanmu, suna maka Babarodo


Wa aufu bil Ahad

Haka Rabbi Ya ce, maza je ka duba


A kundi ka tarad-

Da faɗinSa Ilahi ba ka musa ba


Hakan kuma in Arad-

Ta, sani nasa ba wahala yake ba


Ina yi ma tuni

Duka alƙawarinka da kai ka ɗauka


Ka kwana cikin sani

Lallai ka cika kafin ka sauka


Abinci da magani

Fa suna nema su fi kan talakka


Shin Baba kana gani?

Fa farashin fetur ya ƙi sauka


Ka tuno da batun tsaro,

Da ka ce ba shakka za shi samu?


Tashar ruwa can Baro

Ka ce mana zaka yi kar mu damu


Lantarki tasgaro

Nasa, ka ce zaka cire shi kanmu


Ka ce mana aiyuka

Ga matasa kowa za shi sāma


Birni har ƙauyuka

Hanyoyi ka ce, mun tuna ma


Darajar Naira haka

Ka ce sai ta kamo Dala ma


Da rifainare duka

Gyaransu ina daɗa dai tuna ma


Harkar noma

Da kai ta faɗi, yau Baba ina ta dosa?


Ilimi, ƙasa har sama

Shin wai harkar ga ina ta nausa?


Ƙasar nan tai kama

Da a ce fim ne da ake da wasa


Rashawa, ta'adin kuɗi

Ka ce ba mai kuma yin sa, Baba


Kai ne fa kake faɗi

Ka ja layi ko baka faɗi ba?


Ka sha yin gargaɗi

Sai dai ba ka ɗau hanyar hani ba


To ko dai sai baɗi,

Sannan za kai aikinka Baba?


Har ka fi rabi

Cikin shekarun mulkinka; kana tunawa?


Ka yi wa Allah ka bi

Duk alƙawarinka ka zam cikawa


Ka daure ka yi zubi

Don ko su Wa'e basa iyawa


Ni dai ga shawara

Na baka ka zam ɗaukarta yanzu


Ha'inci, damfara

Su ke hana duk mulki ya wanzu


Ka yi nesa da yaudara

Ita ce ta kashe wancan na dazu


A kul ka bi gambara

Mai saurarenta yana awazzu


Naso ke ma tuni

Don so da ganin girma da ƙauna


Allah ma Ya sani 

Talakawa duk sun yanke ƙauna


Mun yi maka lamuni

Kuma zamu taya ka ka yaƙi 'barna


©Nasir Ahmad Sadiq

      (Mamman Naso)

        

Comments